Connect with us

Labarai

An haramta gidajen giya a Katsina

Published

on

Karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina ta sanyar dokar rufe dukkanin gidajen barasa dake karamar hukumar.

Cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in walwala da jin dadin al’umma na karamar hukumar Abdullahi Umar Danja a madadin shugaban karamar hukumar ta bayyana cewa gidajen barasa sun saba da sashe na 150 na kundin shari’ar Musulunci ta jihar Katsina.

Sanarwar ta kara da cewa gidajen da dokar zata fara aiki ne da gidajen Barasa na Maria da Coach dake Mararrabar Kankara a karamar hukumar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!