Labarai
An kammala shirye-shiryen dawo da mahajjatan jihar kano zuwa gida Najeriya

Amirul Hajj na Jihar Kano, Sarkin Gaya, Dakta Aliyu Ibrahim Abdulkadir, ya tabbatar da cewa an kammala shirye-shiryen dawo da mahajjatan jihar kano zuwa gida Najeriya bayan nasarar kammala aikin Hajjin shekarar 2026.
Amirul Hajj tare da mataimakinsa Alhaji Muhammad Mahraz Karaye da wasu jami’an Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano sun kai ziyara ga jami’an kamfanin jiragen saman da za suyi zirga zirgar domin tattauna batutuwan da suka shafi jigilar mahajjatan zuwa Kano.
Da yake jawabi yayin ziyarar, Dakta Aliyu Ibrahim Abdulkadir ya ce hukumar na aiki kafada da kafada da hukumomin da abin ya shafa da kuma kamfanonin jiragen sama domin kammala tsara jadawalin dawowar mahajjatan.
Dakta Aliyu Ibrahim Abdulkadir ya ce nan ba da jimawa ba za a sanar da ranar da lokacin da za a fara jigilar mahajjatan Kano zuwa gida.
You must be logged in to post a comment Login