Coronavirus
An samu karin masu Corona 643 a Najeriya
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/05/President-Muhammadu-Buhari.jpg)
An samu karin mutum 643 wadanda aka gano suna dauke da cutar Corona a jihohi 18 na kasar nan, da kuma birnin tarayya Abuja.
Hukumar dakile cutuka masu yaduwa ta kasa NCDC ita ce ta sanar da hakan a daren Talata ta shafinta na Twitter.
Zuwa yanzu mutum 34,259 ne aka tabbatar sun kamu da cutar a Najeriya, mutum 13,999 daga ciki sun warke, sai mutum 760 da suka rasa ransu sanadiyyar ta.
Masu cutar Corona 19,500 ne ke ci gaba da jiyyar cutar yanzu haka, a Najeriya.
You must be logged in to post a comment Login