Labarai
An sanya wa sabon babban titin Legas zuwa Calabar sunan Tinubu

Gwamnatin Najeriya ta sanya wa babban titin gaɓar teku – da ya tashi daga Legas zuwa Calaba – sunan shugabana ƙasar Bola Tinubu.
Ministan ayyuka na ƙasar, David Umahi ya ce gwamnati ta ɗauki matakin ne domin nuna yabo ga hangan nesan shugaban ƙasar game da aiki.
Ya ce ma’aikatar ayyuka ta ƙasar ce ta yanke shawarar sanya wa titin sunan shugaban ƙasar, bayan tuntuɓar jagororin ma’aikatar.
Yayin da yake jawabi a taron manema labarai a Abuja, David Umahi ya ce Shugaba Tinubu ya amince da faɗaɗa aikin titin da kilomita 400.
Babban titin wanda ya ratsa jihohin Najeriya aƙalla tara ke bakin gaɓar ruwa zai an tsara zai laƙume kuɗi naira tiriliyan 15.
Titin mai tsawon kilomita fiye da 700 zai tashi daga Legas da kudu maso yammcin ƙasar, zuwa Kalaba da ke kudu maso kudancin ƙasar.
You must be logged in to post a comment Login