Labarai
Ana ci gaba da zanga‑zangar ƙyamar baƙi a sassa da dama na Afirka ta Kudu

An fara zanga‑zangar ƙyamar baƙi a sassa daban‑daban na Afirka ta Kudu, lamarin da ya sa aka jibge jami’an tsaro saboda fargabar rikice‑rikice.
Shugaba Cyril Ramaphosa ya buƙaci masu zanga‑zangar su guji tashin hankali, yana mai jaddada cewa dole ne a gudanar da zanga‑zanga cikin lumana ba tare da tsoratarwa ba.
Zanga‑zangar na da alaƙa da wa’adin da wasu ƙungiyoyi suka bai wa baƙin da ba su da takardu su fice daga ƙasar.
Hakan ya sa mutane da dama suka fara tserewa saboda tsoron hare‑hare, yayin da hukumomi suka ce an riga an mayar da sama da mutum 25,000 kasashensu, yawancinsu daga wasu ƙasashen Afirka.
A birnin Johannesburg, inda ake gudanar da wasu daga cikin zanga‑zangar, an samu tsaiko a harkokin yau da kullum, inda shaguna da dama suka rufe, kuma aka samu yanayi na tsoro da shiru.
Dubban baƙi kuma na cigaba da jiran a kwashe su a sansanonin wucin gadi domin tsira da lafiyarsu.
You must be logged in to post a comment Login