Labarai
Gwamnatin tarayya za ta ci gaba da kwaso mutanen da ke Afirka ta Kudu

Gwamnatin tarayya ta ce za ta ci gaba da kwaso ’yan ƙasar daga Afirka ta Kudu, inda ake samun fargabar hare-haren ƙyamar baƙi dab da zanga-zangar da ake shirin yi a gobe Talata 30 ga Yuni.
Rahotonni sun bayyana An ce wani jirgin Air Peace ya tashi daga kasar nan a safiyar yau Litinin, tare da shirin kwaso wasu daga cikin ’yan ƙasar nan zuwa Legas.
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Najeriya Kimiebi Ebienfa, ne ya bayyana hakan inda ya ce wannan mataki na daga cikin shirin gwamnati na ba da dama ga ’yan ƙasar nan da ke son dawowa gida cikin aminci.
Bayanai sun tabbatar da cewa fiye da ’yan Najeriya 700 na maƙale har yanzu a Afirka ta Kudu, kwanaki kaɗan kafin wa’adin da wasu ƙungiyoyin masu ƙyamar baƙi suka bayar ya cika.
You must be logged in to post a comment Login