Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Ana cigaba da gwajin Corona gida-gida a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano tace ta fito da tsarin bi gida-gida don daukar samfurin gwajin cutar sarke numfashi ta Covid-19, yayinda take ganin hakan zai taimaka wajen magance yaduwarta a tsakanin al’umma.

Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi a taron kaddamar da shirin gwajin cutar, wanda ya gudana a unguwar Wambai dake karamar hukumar Gwale.

Gwamna y ace akwai bukatar magance yaduwar cutar Covid-19 a tsakanin al’umma, wanda hakan ne ya sanya gwamnatinsa bullo da shirin gwaji cutar gida-gida.

Tun farko a nasa jawabi yayin taron, daya daga cikin jami’an kwamitin kar ta kwana kan yaki da annobar Covid-19 a jihar Kano, Dakta Tijjani Hussain ya ce a yanzu haka sun fara gwajin cutar gida-gida a karamar hukumar Birni da kewaye.

Wakiliyar Freedom Radio a fadar gwamnatin Kano Zahra’u Nasir ta ruwaito Dakta Hussain na cewa a gwajin da suka fara yi sun gano cewa ana samun raguwar masu dauke da cutar Covid-19 a jihar Kano.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!