Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Covid-19 Gwamnatin Kano ta ja hankalin jama’a kan tsaftar muhalli

Published

on

Hukumar lura da asibitoci da dakunan binciken lafiya masu zaman kansu ta jihar Kano ta bayyana cewa babu mamaki idan har aka dade ba a gano maganin warkar da cutar corona ba duk kuwa da kokarin yin haka da masana a fadin duniya suka dukufa wajen ganp maganin nata.

Shugaban hukumar, Dakta Usman Aliyu ne ya bayyana haka a cikin shirin ‘Barka da Hantsi’ na tashar Freedom Radio.

Dakta Usman Aliyu wanda ya ce har yanzu masu bincike na duniya sun gaza gano maganin wannan cutar, ya ja hankalin jama’a da su kara lura sosai da kuma samarwa kansu kariya domin kaucewa kamuwa da cutar.

Usman Aliyu wanda kuma kwararren likita ne ya bukaci dukkan ma’aikatan asibtoci a jihar Kano da su tabbatar da marasa lafiya na samun irin kulawar da ta kamace su musamma ma a wannan lokacin da ake fama annobar Covid-19.

Shugaban hukumar ya ja hankalin jama’a kan tsaftar jiki da ta muhallansu da kuma yin amfani da shawarwarin jami’an lafiya don kare kawunansu daga cutuka masu saurin yaduwa, ba wai Covid-19 kadai ba.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!