Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

COVID-19: An bude gidajen kallo a Kano

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta sahale a bude gidajen kallo kasancewar yana taimakawa wajen habaka tattalin arziki.

Gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana hakan a yau lokacin da yake ganawa da shugabannin kungiyar masu gidajen Kallo a fadar Gwamnatin Kano.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya kuma yi kira a gare su dasu bi dukkan kaidojin cutar duba da yadda ake tara matasa a gidajen, a don haka ne ma ya basu safar baki da hanci dubu 40 domin rabawa a gidajen kallon nasu.

Covid-19: An gudanar da sallar Juma’a ta farko a jihar Kaduna

Ana cigaba da gwajin Corona gida-gida a Kano

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron da gwamna, shugaban kungiyar masu gidajen kallo na jihar Kano Sharu Rabiu Ahlan ya ce za su bi dukkan kaidojin cutar adon haka ne ma ya godewa gwamnatin ta Kano bisa wannan dama.

Wakiliyar mu Zahra’u Nasir ta ruwaito cewa kafin ganawa da kungiyar ma su gidajen kallon gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya kuma bukaci masu ruwa da tsaki a jamiyyar APC da su kasance masu wayar dakan alummar su akan bin kaidojin cutar Corona yayin da yake zantawa da su a yau.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!