Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Ana iya magance cutar kuturta- Ma’aikatar lafiya

Published

on

Hukumar yaki da cutar tarin fuka da kuturta da kuma gymbon ciki ta kasa a Nijeriya ta ce kuturta cuta ce da za a iya magance ta tun kafin ta yi kamari, ta hanyar amfani da magungunan kashe kwatoyin cuta.

Shugaban hukumar Dr Chukwuma Anyaike ne ya bayyana hakan ga menma labarai jiya a Abuja, yayin taron bikin ranar yaki da cutar kuturta ta duniya da aka gudanar jiya.

Dr Chukwuma Anyaike ya ce an samar da magungunan kashe kwayoyin cutar da ke haddasa kuturta a duniya, wadda ake fatan ganin karshenta daga nan zuwa shekarar 2035.

Majalisar dinkin duniya ce ta ware duk ranar lahadin karshe ko wane wata domin gudanar da bikin, da nufin fadakar da al’umma hanyoyin kare kai daga cutar kuturta.

Taken bikin na bana shi ne a tashi tsaye don kawar da cutar kuturta.

Rahoto: Abdulkarim Muhammad Abdulkarim

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!