Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Ana samun karuwar masu ciwon kunne a Kano: Dakta Mustapha Sa’idu Salihu

Published

on

Wani likita a sashen kula da lafiyar kunne magkwgaro da hanci a asibiti kwararru na Murtala Muhammad dake Jihar Kano ya bayyana cewa saka tsinke da wasu mutane keyi da sunan sosa kunne, ko kuma saka wani abu mai kaifi a cikin kunnen na haddasa ciwon kune.

Dakta Mustapha Sa’idu Salihu ne ya bayyana hakan a wani bangare na bikin rana kunne ta duniya da majalisar dinkin duniya ta ware, da akeyi duk ranar uku ga watan Maris na kowace shekara a matsayin rana kula da lafiyar kune.

Likitan ya kara da cewa ‘yawaita zama guraren dake da sauti mai karfi na jawo kurumta musamman ga wadanda suke yawaita jin kida a babbar sifika, ko amfani da na’u’rar jin sauti, wato iyafes’.

A don hakan Dakta Mustapha ‘ya ja hankali al’umma da su rinka zuwa ana duba lafiya kunnen su duk shekara’ don gujewa matsala.

A wani bangare na bikin ranar kuma, an gudanar da duba masu matsalar kunne kyauta, tare kuma da basu magunguna a asibiti kwararru na Murtala Muhammad din a yau.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!