Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Asibitin Aminu Kano ya raba maganin ciwon kunne kyauta

Published

on

Shugaban shashin ciwon kunne na asibitin Malam Aminu Kano Dakta Abdulhakim Aluko ya ja hankalin iyayen yara da malam makaranta da su rika kula da lafiyar kunnen yaransu.

Ya ce mutane da yawa suna fama da matsalar ciwon kunne amma basa son zuwa asibiti a duba lafiyarsu wanda haka ke zama babbar barazana ga lafiyar kunne.

Dakta Abdulhakim Aluko ya bayyana haka ne lokacin bikin ranar Ji ta duniya wanda ya gudana a garin Gurin Gawa dake karamar hukumar Kumbotso a jihar Kano.

Ya kara da cewa sun shirya wannan taro ne domin tunawa da ranar ji ta duniya da kuma yin kwajin ciwon kunne kyauta tare da bayar da magani ga al’ummar garin na Gurin Gawa.

A nasa jawabin Shugaban karamar hukumar Kunbotso Alhaji Kabiru Ado ya nuna farin cikinsa kan yadda aka zabi karamar hukumarsa domin yin wannan taro tare da bayar da tallafin.

Wakilin mu Shamsu Dau Abdullahi ya rawaito cewa yara da tsofaffi da dama ne su kaci gajiyar samu wannan magani kyauta

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!