Labarai
Ana samun nasara a yaƙi da boko haram a Najeriya –Lai Muhammad
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/11/Lai-Mohammed.jpg)
Gwamnatin tarayya ta ce Najeriya na samun nasara wajen yaƙar ayyukan ta’addanci.
Ministan yaɗa labarai da raya al’adu Alhaji Lai Mohammed ne ya bayyana hakan, yayin da yake hira a wani shirin BBC.
Ya ce, hujjar da za ta nuna cewa ana samun raguwar ayyukan ta’addanci a yanzu, shi ne yadda ƴan bindigar ke miƙa wuyan su tare da zubar da makaman su ga jami’an tsaron ƙasar nan a kwanakin nan.
Labarai masu alaƙa:
Rundunar soja ta samu nasarar lalata maboyar ‘yan ta’adda a Zamfara
Ministan ya musanta zargin da ake yi na cewa Najeriya ta gaza, inda ya alakanta hakan da irin rikicin da ake gani a Afganistan a yanzu.
You must be logged in to post a comment Login