Labarai
Ana samun nasara a yaki da rashin tsaro da kaso mafi rinjaye a Najeriya – Ministan Tsaro

Ministan Tsaron kasar nan Christopher Musa ya ce ya zuwa yanzu ana samu nasarar shawo kan matsalar rashin tsaro da kasar nan ke fuskanta da kaso mafi rinjaye.
Ministan tsaron ya bayyana hakan ne a yayin da ya ke zantawa da sashen Hausa na Redion Faransa wato RFI.
Ministan ya ce akwai bukatar al’umma su ci gaba da baiwa jami’an tsaro hadin kai domin yaki da yan ta’adda, baya ga goyon bayan da suke samu daga wasu kasashen duniya.
Jawabin Ministan Tsaron Christopher Musa na zuwa ne yayin da ake cigaba da zanga-zangar lumana a wasu sassan kasar nan sakamakon sace dalibai da malaman makaratu a jihohin Borno da Oyo a baya bayan nan.
You must be logged in to post a comment Login