Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Ana wata ga wata: Akwai yiwuwar Ebola ta ɓulla a Najeriya – NCDC

Published

on

Cibiyar daƙile yaɗuwar cutuka ta ƙasa NCDC ta ce, akwai yiwuwar ɓarkewar annobar Ebola a ƙasar nan.

Hakan na cikin wata sanarwa da NCDC ta fitar ta shafinta na intanet mai ɗauke da sa hannun shugabanta Dr. Chikwe Ihekweazu.

Hakan dai na zuwa ne bayan da ƙasar Guine ta shiga fafutukar kawar da cutar daga ƙasar.

A ranar 14 ga watan Fabrairun da muke ciki ne ƙasar Guinea ta sanar da ɓarkewar cutar ta Ebola a ƙasar, lamarin da ya haifar da mace-macen jama’a a yankin N’zerekore na ƙasar.

NCDC ta ce, la’akari da kusancin Najeriya da Guinea ya sanya ta fitar da wannan sanarwa.

Saboda haka ta shawarci al’umma da su rinƙa wanke hannayensu da ruwa da sabulu, sannan a kaucewa ta’ammali da dabbobin daji.

Ana kamuwa da cutar Ebola ne, ta hanyar mu’amala da mai cutar ko taɓa jikinsa, ko guminsa, ko kuma gawarsa.

Haka ma ana kamuwa da cutar ta hanyar amfani da kayan marmari da Jemage ko Birrai suka yi amfani da shi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!