Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Saura ƙiris a sako ɗaliban Kagara – Dr. Gumi

Published

on

Fitaccen malamin addinin Islaman nan Dr. Ahmad Mahmud Gumi ya ce nan ba da daɗewa ba za a sako ɗaliban makarantar Kagara da ƴan bindiga suka sace.

Dr. Gumi ya shiga dajin Kontonkoro domin tattaunawa da ƴan bindigar kan sakin ɗaliban.

Gumi ya ce, tuni ya tattauna da shugabannin ƴan bindigar kan batun satar ɗaliban.

Wasu bayanai sun nuna cewa, tuni gwamnatin jihar Neja da takwararta ta Zamfara suka duƙufa wajen ceto ɗaliban.

Wani shaidar gani da ido ya shaidawa manema labarai cewa jami’an gwamnatin jihar Neja da na Zamfara sun shiga dajin Kotonkoro da ke Dutsin Magaji don tattauna yadda za a sako ɗaliban.

A ranar Laraba ne ƴan bindigar suka kutsa kai makarantar Sakandiren kimiyya ta Kagara da ke jihar Nejan inda suka hallaka guda sannan suka yi awon gaba ɗalibai sama da 40.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!