Connect with us

Labarai

Rundunar Sojin Najeriya sun fatattaki Yan-ta’adda a Zamfara

Published

on

Dakarun sojoji da ke gudanar da aikin kawar da ‘yan bindiga daga garin Bukuyum a jihar Zamfara sun yi artabu da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne da ke ƙoƙarin tserewa a yankin dajin Tsilligidi.

 

Rahotanni sun ce bayan sojojin sun samu bayanan sirri kan motsin ‘yan bindigar, suka nufi maboyarsu.

 

Sojojin sun tare su tare da yin musayar wuta mai tsanani. A yayin artabun, an kashe da dama daga cikin ‘yan bindigar, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga.

 

An bayyana cewa wannan farmaki wani ɓangare ne na ƙoƙarin da sojoji ke yi na rusa sansanonin ‘yan bindiga da kuma dawo da zaman lafiya a al’ummomin da ke fama da matsalar tsaro a jihar Zamfara. Har yanzu dai ana ci gaba da bibiya da share dazukan domin kamo waɗanda suka tsere.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!