Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ba na goyon bayan ƙarin farashin mai – Kawu Sumaila

Published

on

Tsohon mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan majalisar wakilai Abdurrahman Kawu Sumaila ya ce, baya goyon ƙarin farashin mai da gwamnatin tarayya ta yi.

Kawu Sumaila ya bayyana hakan a zantawarsa da Freedom Radio, yana mai cewa, tsarin da gwamnatin tarayya ke bi a yanzu ya saɓa da tsarin da talakawan ƙasa suka zaɓe ta a kai.

“Talakawa sun zaɓi gwamnatin shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ne domin su samu sauyi daga mulkin jam’iyyar PDP, amma sai ga shi har yanzu salon bai canza ba, kasancewar talakan ƙasa na ci gaba da fuskantar matsi da tsadar rayuwa” a cewar sa.

Kawu Sumailan ya ƙalubalanci ƴan kishin ƙasa da magoya bayan shugaba Buhari na haƙiƙa da kuma jam’iyyun adawa kan su fito su nuna rashin amincewar su da yin ƙarin farashin man.

Ku kasance da Freedom Radio da ƙarfe 6 na safiyar gobe Alhamis domin jin cikakken labarin a shirin mu na An Tashi Lafiya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!