Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ba shiga ba fita a Gombe daga gobe Alhamis

Published

on

Gwamnatin jihar Gombe ta sanya dokar zaman gida da takaita cakuduwar jama’a daga karfe 6 na yammacin gobe zuwa karfe 7 na safe domin dakile yaduwar cutar Coronavirus.

Gwamnan jihar Muhammadu Inuwa ne ya bayyana hakan ta cikin jawabin da ya gabatar a yammacin yau, inda ya ce gwamnati ta rufe dukkanin kasuwannin jihar da sauran tarukan jama’a na bukukuwa ko al’ada ko na ibada.

Wakilin mu Usman Abubakar Usmaniyya ya rawaito mana cewa gwamnan jihar ta Gombe ya dakatar da dukkan wata zirga-zirga daga wannan karamar hukumar zuwa wata karamar hukuma ba.

Sannan gwamnan ya ce dokar ba ta shafi masu ayyuka na musamman ba.

A kididdigar baya-bayan nan da cibiyar dakile cutuka masu yaduwa ta kasa NCDC ta fitar ta ce izuwa yanzu mutane biyar suka kamu da cutar a jihar Gombe

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!