Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Za’a ci gaba da gwajin cutar Corona a Kano

Published

on

A yau Asabar Asibitin Aminu Kano ya rufe sashin da ake gwajin cutar Covid-19 a jihar Kano sakamakon feshin maganin kashe kwayoyin cutuka da akai a gurin.

Shugaban sashin gwajin Cutar Corona a Asibitin Aminu Kano Dakta Nasiru Magaji Sadik ne ya bayyna hakan a zantawar sa da mai Magana da yawun Asibitin Hajiya Hauwa Muhammad, game da dalilan da suka sanya aka rufe bangaren.

AKTH ya samu nasarar gudanar da aikin kwakwalwa karo na biyu

Dakta Nasiru Magaji ya kuma ce sun rufe gurin ne sanadiyyar feshin kasha kwayoyin cutuka da akai, wanda kuma zai dauki akalla awanni arba’in da takwas kafin a ci gaba da amfani da gurin.

Ya kuma ce da zarar lokacin da aka dibawa wajen da aka gudanar da feshin ya cika za’a ci gaba da gwada mutanan da ake zargin na dauke da cutar ta Covid-19.

A ziyarar da Freedom Radiyo ta gudanar a Asibitin na Aminu Kano ta lura cewa babu kowa a gurin da ake gudanar da gwajin cutar ta Covid-19 inda gurin ya kasance a kulle.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!