Connect with us

Labarai

Ba zan taɓa yarda a halatta amfani da Wiwi a Kano ba – Ganduje

Published

on

Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ce, Kano ba zata goyi bayan halasta amfani da tabar wiwi ba.

Gwamnan ya bayyana hakan ne, yayin da ya karɓi baƙuncin shugaban hukumar NDLEA na ƙasa Janar Buba Marwa Mairitaya.

A jawabinsa, Gwamna Ganduje ya nanata cewa jihar Kano ba zata amince da kiraye-kirayen da wasu ɓangarorin ƙasar nan ke yi ba, na neman a halasta ta’ammali da Wiwi.

Ya ce, al’ummar Kano ba su da wata buƙata game da hakan, don haka kada ma a soma tunkararsa da wannan batun.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!