Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Babbar kotun daukaka kara ta umarci yan sanda su cafke Abdullahi Abbas tare da bincikarsa

Published

on

Babbar kotun daukaka kara a jihar Kano, ta umarci kwamishinan ‘yan sandan da ya gudabar bincika tare da kama shugaban jam’iyyar APC na jihar Kano Alhaji Abullahi Abbas, bisa zarginsa da zagi hadi da barazanar kisa ga Muhammad Lamido.

Sai dai bayan nadar muryar shugaban jam’iyyar Muhammad Lamido ya yi lokacin da yake cin zarafin sa, Lauyan sa Barister Bashir Yusuf Tudun Wuzurchi ya shigar da kara a gaban kotun Mai shari’a A.S. Ambode, inda alkalin ya umarci kwamishinan ‘yan sandan da ya yi bincika tare da cafke Abdullahi Abbas.

A zantawarsa da Freedom radio Barister Bashir Yusuf Tudun Wuzurchi, ya bayyana dalilan da suka sanya wanda yake karewa daukar matakin shari’a.

Latsa nan domin sauraron lauya

https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2023/02/APC-KOTU-AN-TASHI-LAFIYA-02-02-2023.mp3?_=1

Sai dai duk kokarin ji daga bakin Abdullahi Abbas kan wannan lamari hakan mu ya ci tura, amma da zarar ya magantu zaku ji mu da shi.

Mai shari’a A.S. Ambode ya kuma sanya ranar 16 ga wannan watan da muke ciki na Faburairu domin ci gaba da sauraron shir’ar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!