Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Wasu cikin jami’an gwamnati a fadar Villa na yi wa Tinubu zagon kasa- El-rufai

Published

on

Gwaman jihar Kaduna Malam Nasiru El-Rufai, ya ce, akwai wasu jami’ai a fadar gwamnatin tarayya ta Aso Villa da ke birnin tarayya Abuja da sike yi wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Asiwaju Bola Tinubu, zagon kasa domin ya fadi a zabe.

Gwamnan, ya bayyana hakan ne ta cikin wani shirin safe na gidan Talabijin na Channels.

Ya ce, wadannan mutanen da bai bayyana sunayensu ba suna cike da takaicin yadda Tinubu ya doke ‘yan takararsu a zaben fidda gwani, son haka suka shiga shirya makarkashiya domin ya fadi zaben.

El-Rufai ya kuma ce, mutanen na fakewa ne da muradin shugaban kasa Muhammadu Buhari na yin abin da yake ganin ya dace.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!