Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

CAF za ta tsayar da matsaya a kan wasannin Champions League

Published

on

Masu ruwa da tsaki a harkokin kwallon kafa a Afrika za su yanke hukunci kan ci gaba da gasar Champions League da kuma gasar cin kofin kalubale na Afrika a wannan watan na Satumba da muke ciki a kasar Morocco duk da cutar COVID-19 da tayi kamari a yankin.

Kasar ta Morocco ce dai za ta karbi bakuncin zagaye na farko a wasan kusa da na karshe a gasar ta Champions League da kuma wasannin kungiyoyi hudun karshe da za su fafata a gasar cin kofin kalubale a wannan watan na Satumba.

Jami’an hukumar kwallon kafa ta Afrika na nuna damuwar su duba da yadda annobar COVID-19 ke ci gaba da yaduwa a kasar ta Morocco.

A kalla 12 daga cikin ‘yan wasan kungiyoyi 16 da suke fafatawa a gasar Botola Pro 1, wadanda a ka samu masu cutar Corona, lamarin da ya saka dole ‘yan wasa ke zama a Otel ko a sansanin wasa, maimakon komawa gida a duk lokacin da a ka gama kowane wasa.

Ana dai sa ran gudanar da wasannin cin kofin kalubalen ne a ranar 22 ga wannan watan. Inda kungiyar Hassania Agadir ta kasar Morocco za ta kara da Renaissance Berkane ita kuwa Pyramids ta kasar Masar za ta kece raini da Horoya ta kasar Guinea.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!