Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

CBN ya musanta bada umarnin ci gaba da bayar da tsofaffin kudi a bankuna

Published

on

Central Bank Of Nigeria

Babban bankin Nijeriya CBN, ya ce, har yanzu bai bayar da umarni ga bankunan kasuwanci na su fara bayar da tsofaffin kudi ga kwastomomi ba.

Mai magana da yawun CBN Isa Abdulmumin, ne ya bayyana hakan a zantawarsa da jaridar Daily Trust.

Ya ce CBN bai bayar da wani sabon umarni ga bankunan kasuwanci ba kan hukuncin da kotun koli ta yanke a ranar Juma’ar da ta gabata na bayar da umarnin a rika rarraba tsofaffin takardun kudi ga abokan huldarsu ba.

A ranar juma’ar da ta gabata ne dai kotun kolin Nijeriya karkashin jagorancin mai shari’a Inyang Okoro, ta bayar da umarnin ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kudin har zuwa ranar 31 ga watan Disamban bana.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!