Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

KannyWood

Cibiyar horas da harkar fim ta bullo da hanyoyin bunkasa sana’ar

Published

on

Shugaban sashen horas da dabarun shirya fina-finai, Alhaji Musa Gambo, ya nemi kungiyoyin masu gudanar da sana’ar fim su rinka tura mambobinsu wuararen samun horo domin ciyar da bangaren gaba a Najeriya.

Shugaban ya bayyana haka ne a bikin yaye daliban makarantar da samu horo kan yadda ake shirya fina-finai.

Alhaji Musa Gambo ya ja hankalin daliban da suyi amfani da horon da suka samu wajen tsara fina-finan da zasu dace da al’adun Hausawa da ma sauran al’adun Najeriya.

Karin Labarai:

Halin da ake ciki a Kannywood a wannan mako

Muhimman abubuwan dake faruwa yanzu haka a Kannywood

A cewar sa, gwamnatin jihar Kano na kokartawa don ganin ta bunkasa harkar fina-finai da ma al’adun Hausawa a jihar da ma kasa baki daya.

Wakilin mu Shamsu Da’u Abdullahi ya rawaito cewa daga cikin manyan bakin da suka hallarci taron akwai shugaban hukumar tace fina-finai ta jihar Kano Isma’il Na’abba Afakalla.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!