Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

Corona: El-rufa’i ya bada damar buɗe ƙarin makarantu da Islamiyoyi

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta amince da komawar sauran ɗalibai makaranta a ranar Litinin mai zuwa 22 ga watan Fabrairu, 2021.

Ɗaliban da za su koma makarantar sun haɗar da ƴan aji biyu na ƙaramar Sakandire da aji ɗaya da biyu na babbar Sakandare a makarantun kuɗi da na Gwamnati.

Sai kuma ɗaliban makarantun Firamare baki-ɗaya.

Haka kuma Gwamnan ya amince a koma makarantun Islamiyya a jihar daga ranar Litinin ɗin.

Hakan dai na cikin wata sanarwa da Kwamishinan ilimi na jihar Shehu Usman Muhammad ya fitar a daren Jumu’a.

Sanarwar ta nemi shugabannin makarantun da su shirya ci gaba da karatu a makarantu.

Sannan an nemi kowace makaranta kan ta tabbatar ta bi matakan kariya daga annobar Koronabairos.

Ma’aikatar ilimin ta ce, kwamitin yaƙi da cutar Korona zai sanya idanu domin tabbatar da cewa makarantun sun bi matakan.

Baya ga wannan ma’aikatar ilimin ta shawarci makarantun da su riƙa amfani da hanyoyin fasahar zamani wajen karatu.

Sannan za a ci gaba da karantar da ɗalibai ta hanyoyin rediyo da talabijin domin cike giɓin da aka samu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!