Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Gwamnatin Ganduje za ta kaddamar da gidajen da aka gina wa ma’aika

Published

on

Gwamnatin jihar Kano, za ta kaddamar da gidajen da aka gina domin ma’aikatan gwamnati su mallaka cikin sauki musamman malaman makaranta da za a rika cirar kudin daga albashin su.

Gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ne ya bayyana hakan da yammacin jiya Alhamis lokacin da yake kaddamar da bada shidar daukar Malaman makaranta su dubu daya da dari biyar a dakin taro na Sani Abacha da ke Kofar Mata.

Ganduje, ya kara da cewa gwamnatinsa za ta samar da karin gidajen domin saukaka wa malaman makaranta wajen koyar da dalibai.

Gwamna Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya kuma Jagorancin rantsar da sababbin manyan sakatarorin da ya nada a makon nan da muke ciki.

 

Rahoton: Abba Isah Muhammad

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!