Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Covid-19: BUK ta umarci daliban dake zaune a makarantar su koma gidajen su

Published

on

Jami’ar Bayero dake Kano ta umarci daliban da yanzu haka ke zaune a makarantar da su koma gidajen iyayen su,  su zauna har nan da wata guda.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran jami’ar Lamara Garba, ya fitar yau a madadin magatakardar jami’ar ta Bayero.

Haka kuma sanarwar tace daliban da suke zuwa daukar karatu daga gidajen su su dakata har zuwa lokacin da jami’ar za ta bukaci su dawo makaranta.

Sanarwar ta ce umarnin na zuwa ne bayan da ma’aikatar ilimi ta tarayya ta karkashin hukumar kula da jami’o’I ta kasa NUC, ta fitar da sanarwar cewa, Gwamnatin tarayya ta bada umarnin da’a rufe makarantun kasar nan ciki har da jami’o’i, sakamakon barazanar Cutar Corona.

Jami’ar ta ce umarnin zai fara aiki ne daga ranar litinin ashirin da uku ga watan maris din nan da muke ciki.

Ana kuma tsammanin ma’aikatan jami’ar za su ci gaba da gudanar da ayyukan su kamar yadda aka saba.

Sai dai ana shawaratar su da su kiyaye dukkan dokokin da masana kiwon lafiya ke bayarwa don gudun kamuwa da cutar covid-19.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!