Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Covid-19: Rundunar ‘yan sandan Kano ta dakatar da karbar korafi baka-da- baka

Published

on

Rundunar yansandan Jihar Kano ta ce za ta rinka karbar korafin da yazamo dole ne kawai ta wayar Salula domin kaucewar yaduwar cutar Korona a fadin jihar Kano.

Komishinan Yansandan Kano CP Habu Ahmad Sani, ne ya bayyana hakan ta bakin mai magana da yawun ‘yan sandan Jihar Kano DSP Abdullah Haruna, a yayin zantawarsa da wakilin mu Abba Isah Muhammad, a shelkwatar rundunar dake Unguwar Bomfai a nan Kano.

Abdullahi Haruna, ya kara da cewar sun dauki wannan mataki ne domin yaki da yaduwar cutar korona.

DSP Abdullahi Haruna, ya kuma kara da cewar idan ya zamo dole sai mutum ya kawo korafi kafa da kafa to wajibi ne yazo shi kadai maimakon gayyato abokansa.

Wakilinmu Abba Isah Muhammad, ya ruwaito cewa Rundunar ‘yansandan ta Jihar Kano ta sallami wandanda ake zargi da aikata kananan laifuka ta hanyar bayar dasu beli zuwa wani lokaci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!