Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Covid-19: Sarkin Saudiya ya killace kansa

Published

on

A kalla iyalan gidan Masarautar Saudiya 150 sun kamu da cutar Corona Virus da suka hada da gwamnan birnin Riyadh wanda yanzu haka ke kwance a sashen kula da marasa lafiyar da ke cikin matsanancin hali a asibiti, kamar yadda Jaridar New York Times ta Amurka ta rawaito.

Likitocin da ke kula da iyalan gidan sarautar sun samu takardar umarnin ware gadaje a kalla 500 a asibitin Sarki Faisal saboda yiwuwar samun karin mutane daga gidan sarautar dauke da cutar.

LABARAI MASU ALAKA

Covid-19 Gwamnatin Saudia zata bude ofishin Fasfo

Kasar Saudiya ta dakatar da zuwa Umara

An gargadi maniyyata guzurin ababan da aka hana a kasar Saudiya

Masarautar Saudiyar ta bai wa asibitin umarnin fitar da duk wani mara lafiyar da ke cikin matsanancin hali domin tanadar gadaje ga iyalan masarautar.

Rahotanni sun ce, yanzu haka Sarki Salman mai shekaru 84 ya kebe kansa a can wata fadarsa da ke kan tsibirin tekun Maliya a kusa da birnin Jeddah, yayin da Yarima Mai Jiran Gado, Mohammed bin Salman ya kwashi ministocinsa don komawa wani sashi na tsibirin, inda ya yi alkawarin gina sabon birni mai suna Neom.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!