Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Da ɗumi-ɗumi: Sarkin Katsina ya kori Hakimi kan taimakawa Ƴan bindiga

Published

on

Mai Martaba Sarkin Katsina Alhaji Abdulmumin Kabir Usman ya kori ɗaya daga cikin hakimansa, sakamakon samun sa da hannu dumu-dumu wajen taimakawa ƴan ta’adda.

Masarautar Katsina bisa sahalewar Gwamnatin jihar ta tsige tare da korar Sarkin Fawar Katsina Hakimin Ƙanƙara Alhaji Yusuf Lawan.

Sakataren Masarautar Alhaji Bello Mamman Ifo ne ya tabbatar da hakan, a zantawarsa da wakilin Freedom Radio Yusuf Ibrahim Jargaɓa a daren Jumu’ar nan.



Ya ce, hakan ya biyo bayan kammala bincike da kwamitin da masarautar ta kafa yayi a kan hakimin.

Alhaji Bello Mamman ya ƙara da cewa, binciken da aka yi ya tabbatar da ƙorafe-ƙorafen da aka yi a kan hakimin, na yin haɗin kai da ƴan bindiga.

Yanzu haka dai tuni Masarautar Katsinan ta fara shirin domin maye gurbin sa a cewar sakataren.

Jihar Katsina dai na cikin jihohi Arewa da ke fama da matsalar ƴan bindiga masu garkuwa da mutane.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!