Labarai
Dakarun OPEP sun dakile yunkurin ’yan bindiga na kai hari a Filato

Dakarun Rundunar Operation Enduring Peace, OPEP,sun dakile wani yunkurin wasu ’yan bindiga da ake zargin mayakan Berom ne, na shirin kai hari kan wasu al’ummar Fulani a ƙaramar hukumar Mangu ta jihar Plateau.
Rahotanni sun ce dakarun sun samu bayanan sirri kan yadda ƙungiyar ke tahowa daga Barkin Ladi zuwa yankunan Gwomgada, Dorong da Kaduno, lamarin da ya sa rundunar ta gaggauta tura dakarunta domin dakile harin.
Sojojin sun yi arangama da ’yan bindigar a yankunan Makera da Kaduno, inda suka tilasta musu ja da baya zuwa ƙaramar hukumar Jos ta Gabas.
A halin yanzu, rundunar ta ce dakarunta na ci gaba da bin sawun ’yan bindigar, yayin da aka kuma tura jami’an
You must be logged in to post a comment Login