Labarai
Dakarun Operation Fansan Yamma sun dakile yunkurin garkuwa da mutane a Kaura Namoda

Dakarun sojin kasar nan na Operation Fansan Yamma, sun dakile wani yunkurin yin garkuwa da mutane a ƙauyen Unguwar Rogo, a ƙaramar hukumar Kaura Namoda ta jihar Zamfara.
Rundunar ta ce sojojin sun ceto fararen hula tara, ciki har da jariri, bayan ’yan bindiga sun yi wa mutanen da ke tafiya a wata hanya kwanton bauna.
Mai magana da yawun rundunar, Laftanar Kanal Aliyu Danja, ya ce ’yan bindigar sun buɗe wa motocin da ke wucewa wuta daga cikin wata gonar gero, da nufin yin garkuwa da mutanen da ke cikinsu.
Ya ce sojojin da aka aika wurin bayan samun kiran neman agaji sun yi artabu da ’yan bindigar, lamarin da ya tilasta musu tserewa zuwa cikin daji.
A cewar rundunar, mata biyu sun samu raunukan harbin bindiga a yayin harin, kuma an kai su asibiti domin kula da lafiyarsu.
You must be logged in to post a comment Login