Labarai
Yan Zambiya na kada kuri’a a zaɓen shugaban ƙasa da ƴan majalisar dokoki

Al’ummar Zambiya na gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ƴan majalisar dokokin ƙasar.
Ana kallon zaɓen a matsayin ma’aunin gwajin ingancin dimokuraɗiyya a ƙasar mai tarihin ‘ɗorewar tsarin dimokuraɗiyya a Afrika.
Shugaban ƙasar Hakainde Hichilemana wanda ke neman wa’adi na biyu na da farin jini sakamakon rawar da ya taka lokacin da ƙasar ke fama da matsin tattalin arziki.
Ana ganin za a fafata ne tsakanin shugaban ƙasar da jagoran adawa Brian Mundibile wanda magoya bayan tsohon shugaban ƙasar Edgar Lungu ke mara wa baya.
Ɗan takarar shugaban ƙasa dai na buƙatar sama da kashi 50 na ƙuri’u kafin ya yi nasara.
You must be logged in to post a comment Login