Labarai
Jam’iyyar APM ta lashe kujerun shugabannin kananan hukumomi 20 a Bauchi

Jam’iyyar APM mai alamar Rogo ta lashe dukkan kujerun shugabannin kananan hukumomi 20 a zaben da aka gudanar a Jihar Bauchi ranar Litinin.
Shugabar Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Bauchi, BASIEC, Jummai Abubakar, ce ta sanar da sakamakon zaben a daren Litinin. Ta ce APM ta kuma lashe kujerun kansiloli 319.
Sai dai jam’iyyun SDP, NRM, ZLP da YPP sun samu kujerar kansila daya kowannen su.
Tun ranar Lahadi ne wasu jam’iyyun adawa suka sanar da kauracewa zaben, suna zargin an shirya shi ne domin fifita APM.
Gwamna Bala Mohammed ya bayyana zaben a matsayin wanda aka gudanar cikin lumana, yana mai cewa kauracewar wasu jam’iyyun ba za ta rage sahihancinsa ba. Gwamnatin jihar ta kuma ayyana ranar Litinin a matsayin ranar hutu domin bai wa ma’aikata damar kada kuri’a.
You must be logged in to post a comment Login