Labarai
Rundunar Operation Fansan Yamma ta dakile yunkurin sace mutane tare da ceto mutum 14 da ke tsare

Rundunar Sojin kasar nan ta Operation Fansan Yamma, ta dakile wani yunkurin sace mutane, tare da ceto mutane 14 da aka yi garkuwa da su a karamar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara.
Rundunar ta gudanar da aikin ceton a yau , bayan samun sahihin bayanan sirri kan wasu mutane da ake zargin suna aikata laifuka a kusa da kauyen Magazu.
Bayan samun bayanan sirrin , sojojin sun isa yankin inda suka yi arangama da wasu ‘yan bindiga da ake zargin suna kokarin yin garkuwa da fararen hula, ciki har da masu ababen hawa.
Sojojin sun bude wuta kan ‘yan bindigar, lamarin da ya tilasta musu barin motarsu tare da tserewa zuwa cikin daji.
You must be logged in to post a comment Login