Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Daliban Kano a Sudan sun nemi a dawo dasu gida saboda Coronavirus

Published

on

Kungiyar iyayen dalibai ‘yan asalin jihar Kano dake karantar likitanci a kasar Sudan ta nemi gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje kan ya taimaka musu wajen dawowa da daliban Kano gida daga kasar Sudan.

Shugaban kungiyar iyayen daliban Ahmad Baffa Usman ya bayyana cewa, tuni gwamnatin kasar Sudan ta bada sanarwar rufe jami’o’in kasar gabaki daya saboda cutar ta Coronavirus.

Wanda hakan ya sanya, hukumomin makarantun da dalibai ‘yan jihar Kano suke, suka baya da hutun wata uku, duba da karatowar watan azumi.

Rufe makarantun ya sanya daliban cikin wani hali, a don haka suke neman gwamnan Kano kan ya karasa ladan sa, ya dawo da daliban gida.

Wakilin mu Nasir Salisu Zango ya tuntubi shugaban hukumar bada tallafin karatu ta jihar Kano, Zakari Habu P.A wanda ya ce gwamnatin Kano za tayi iya kokarin ta wajen ganin an share hawayen wadannan daliban.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!