Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Covid-19: An fara rufe makarantun Islamiyya a Kano

Published

on

Hukumar makarantar Islamiyya ta Tahfizul Qur’an dake unguwar Daneji a Kano ta rufe makarantar a ranar Asabar saboda fargabar annobar Coronavirus.

Sakataren makarantar Dakta Ahmad Abdullahi Ibrahim Daneji, ya shaidawa Freedom Radio cewa, sun baiwa daliban makarantar hutu ne ganin yadda gwamnati ta bada umarnin rufe sauran makarantun jihar.

Dakta Ahmad Daneji ya ce sun shaidawa daliban makarantar cewa su zauna a gida na tsawon mako biyu su cigaba da yin addu’o’I, da kuma bin ka’idojin da jami’an lafiya suka bayar.

Wasu daliban makarantar Tahfizul Qur’an Daneji

“Sannan mun sanar da su cewa idan Allah ya sa an samu sauyi, gwamnati ta sanar da wata sanarwa da ta nuna za a cigaba da gudanar da al’amuran yau da kullum, to dalibai su dawo mu cigaba da karatu” a cewar Dakta Daneji.

Karin labarai:

Covid-19: An dakatar da kwallon kafa a Kano saboda Coronavirus

Musulmai sun yi taron addu’a kan Coronavirus a Kano

Makarantar Tahfizul Qur’an Daneji, na cikin manyan makarantu dake da yawan dalibai a kwaryar birnin Kano.

Idan baku manta ba, tuni gwamnatin jihar Kano ta bi sahun sauran gwamnatocin jihohin Arewa cin kasar nan wajen rufe daukacin makarantu saboda fargabar cutar Coronavirus.

Wasu daliban makarantar Tahfizul Qur’an Daneji

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!