Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Daliban Yanzu na sakaci da Karatu – Kungiyar Dalibai

Published

on

BUK 92 Class
  • Kungiyar ta ce ilimi shike gina rayuwar dan Adam
  • Ta bayar Tallafin Kayayyakin karatu
  • Tayi kira ga daliban da su maida hankali wajen samun ilimi ingantacce.

Mai bada shawara kan harkokin shari’a a kungiyar tsoffin daliban Jami’ar Bayero ta Kano aji na 1992, Barista Sa’idu Muhammad Tudunwada ya koka game da sakacin dalibai a harkokin karatun su.
Barista Sa’idu ya bayyana hakan ne a zantawarsa da wakilin Freedom Radio Nura Bello da safiyar yau.
Ya ce ‘kungiyarmu na bayar da gudunmawar kaya da kuma da tallafin karatu ga dalibai marasa karfi’.
A nasa bangaren Mudi Adamu wanda mamba ne a kungiyar, ya ce “muna tallafawa abokan karatunmu wadanda suke cikin matsala da ma wadanda suka rasu kuma iyalansu suna bukatar tallafi.”
Kungiyar ta yi kira ga dalibai da su mayar da hankali wajen koyon ilimi mai inganci don gina rayuwarsu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!