Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Dalilan da suka sanya gwamnatin Kano daukar alarammomi aikin koyar wa – Ganduje

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da daukan alarammomi sittin da za su koyar a makarantu goma sha biyar da gwamnatin ta samar don koyar da almajirai ilimin zamani.

Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ne ya amince da hakan a jiya Litinin.

Amincewar ta biyo bayan karbar rahoto daga hukumar da ke kula da makarantun Isalamiyya a jihar Kano, karkashin jagorancin kwamishinan Ilimi Malam Muhammad Sunusi Kiru.

Gwamna Ganduje ya ce, gwamnatin sa ta samar da kwamitin da zai magance matsalar hana barace-barace a kan titinan jihar Kano, wanda kuma ta tsara samar da makarantun da za su bai wa almajiran damar hadar Alqur’ani mai da na zamani don kyautata rayuwarsu.

Idan dai za a iya tunawa gwamnatin ta samar da makarantun a kananan hukumomin Bunkure da Madobi da Bagwai da kuma sauran kananan hukumomi goma sha biyu cikin kananan hukumomin Arba’in da hudu na fadin jihar Kano.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!