Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Ganduje zai dauki alarammomi 60 domin koyar da almajirai a Kano

Published

on

Hukumar kula da tsangayun Islamiyya ta Jihar Kano ta ce, za ta dauki alarammomi sittin domin ci gaba da koyar da almajiran da aka dawo mata da su daga wasu jihohin Kasar nan.

Shugaban hukumar Gwani Yahuza Gwani Dan-Zarga ne bayyana haka yau, a lokacin da take tantance alarammomin a shalkwatar hukumar da ke nan Kano.

Shehin Malamin ya kuma ce, gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya baiwa hukumar umarnin baiwa almajiran ilimin addini da na zamani yadda ya kamata.

Gwani Yahuza Gwani Dan-Zarga ya kuma ce, makarantu goma-sha shida ne za a tura alarammomi domin karantar da almajiran karatun boko da na zamani.

Wakilin mu Bilal Nasidi Mu’azu ya ruwaito cewa, alarammonin da za a dauka don koyarda da daliban sun fito ne daga kananan hukumomin Jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!