Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rundunar sojin Najeriya ta karyata rahoton Majalisar Dinkin Duniya kan kisan manoma

Published

on

Rundunar sojin Najeriya ta nanata cewa manoma 43 aka kashe, ba 110 da Majalisar Dinkin Duniya ta ce an kashe ba.

Mai Magana da yawun rundunar, John Enenche a wata hira da ya yi da gidan talibijin na Channels, ya ce har yanzu suna tattara bayanai kan mutanen da harin ya shafa domin tabbatar da adadin wadanda suka mutu.

Sai dai rundunar ta ce abinda yake kara ta’azzara batun matsalar tsaro shine, yadda mazauna yankunan da ke fama da tashe-tashen hankula ba sa kai rahoto ga sojoji da sauran hukumomin tsaro kan halin da suke ciki.

“Mutane da dama basa kawo mana rahoton abinda ke addabar su kan sha’anin tsaro, kuma ba dole bane ka tilastawa mutane su sanar maka abinda ke faruwa.” In ji shi

Ko da yake John Enenche ya ki bayyana yanda rundunar sojin ke tattara bayanata akan wuraren da fama da yake-yake a arewacin Najeriya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!