Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

Dalilin da ya sa muka dakatar da Kwankwaso daga jam’iyya – PDP

Published

on

Jam’iyyar PDP ta dakatar da tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso tana mai zargin sa da hannu a rikicin da ya faru a yayin zaben shugabannin shiyyar arewa maso yamma wanda ya gudana a garin Kaduna a makon jiya.

 

Bayanin dakatarwar na kunshe ne cikin wata wasika da tsagin jam’iyyar da ke biyayya ga tsohon ministan kasashen wajen kasar nan Ambasa Aminu Wali, ya fitar.

 

Takardar dakatarwar na dauke ne da sanya hannun sakataren tsagin shugabancin da ke biyayya ga Aminu Wali, H. A Tsanyawa.

 

Rahotanni sun ce jam’iyyar PDP a jihar Kano dai ta dare gida biyu, inda daya bangaren shugabancin ke biyayya ga tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, yayin da daya bangaren ke biyayya ga Aminu Wali.

 

A yayin taron zaben sabbin shugabannin shiyyar arewa maso yamma da ya gudana a garin Kaduna a ranar asabar ta makon jiya, an yi ta bata kashi tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar wanda ya kai ga farfasa akwatunan zabe da takardun kada kuri’a.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!