Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Duk wanda ba shi da lambar NIN zai fuskanci daurin shekaru 14 – Pantami

Published

on

Ministan sadarwa Dr Isa Ali Pantami, ya ce, duk wani dan Najeriya da ba shi da lambar shaidar zama dan kasa (NIN) zai iya fuskantar daurin shekaru goma sha hudu a gidan gyaran hali.

Dr Isa Ali Pantami ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai da kwamitin kula da sadarwa na shugaban kasa ya saba gudanarwa a duk mako.

Ya ce ya zuwa jiya laraba talatin da daya ga watan jiya na Maris,‘yan Najeriya miliyan hamsin da daya ne suka yi rajistar lambar ta NIN.

‘‘Ina tabbatar muku cewa duk dan Najeriya da ya yi sakaci bai mallaki lambar shaidar dan kasa (NIN) ba, to zai iya fuskantar daurin shekaru goma sha hudu, kamar yadda ya ke a kundin tsarin mulkin kasar nan’’ a cewar Pantami.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!