Connect with us

Kiwon Lafiya

Fadar shugaban kasa ta zargi ‘yan siyasa da shirya kashe-kashen manoma da makiyaya

Published

on

Fadar shugaban kasa ta zargi ‘yan siyasa da shirya kashe-kashen da ke faruwa tsakanin manoma da makiyaya a yankin arewa maso tsakiyar kasar nan.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan kafofin yada labarai Malam Garba Shehu ya fitar jiya a Abuja.

Sanarwar ta ce akwai wata kullalliya da wasu fusatattun ‘yan siyasa da sukayi wadaka da dukiyar kasar nan tsawon shekaru ke yi na neman raba kawunan al’ummar kasar nan wajen amfani da rikicin manoma da makiyaya.

Malam Garba Shehu ta cikin sanarwar dai, ya kuma ce; jami’an tsaro na aiki tukuru domin zakulo ‘yan siyasar da ke fakewa da makiyaya suna kashe mutane a kasar nan.

A cewar sanarwar kama wasu ‘yan ina da kisa da sojoji su ka yi a jihar Taraba a baya-bayan nan, ya nuna karara cewa ‘yan siyasa ne ke shirya kashe-kashen da ke gudana tsakanin manoma da makiyaya a yankin na arewa tsakiya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!