Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

FIFA Ranking: Najeriya ta ci gaba da rike kambunta a Afrika da Duniya

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagles ta ci gaba da rike matakin da take na 34 a jadawalin da hukumar kwallon kafa ta Duniya FIFA ke fitarwa duk wata na kasashen da suka nuna bajinta.

A jiya Alhamis 16 ga watan Satumbar da muke ciki na shekarar 2021 hukumar ta FIFA ta fitar da jadawalin watan Satumba.

Kalubale ya hana ‘yan wasan Najeriya buga wasanni 100-Enyeama

A Afrika ma Najeriya ta ci gaba da rike matakin da take na 5, yayin da kasar Tunisia take a matki na 25 a Duniya ta 2 kuma a Afrika kasar Senegal ce ta 1 a Afrika ta kuma 20 a Duniya.

Najeriya dai ta yi kokari a watan Satumbar da muke ciki inda ta doke kasar Liberia da ci 2-0 da kasar Cape Verde da ci 2-1 a wasannin neman tikitin buga kofin Duniya da za’a gudanar a kasar Qatar a shekara mai kamawa ta 2022.

Kasar Algeria ce ta 3 a Afrika ta kuma 30 a Duniya sai kasar Morocco ta 4 a Afrika ta kuma 33 a Duniya.

Kasar Belgium ta ci gaba da rike matakin da take na 1 a Duniya sai dai kasar France mai rike da kofin Duniya ta koma mataki na 4 yayin da kasar Brazil ke a matsayin ta 2 sai kasar , England da take a matsayin ta 3 inda kasar Italy ke a matsayin ta 5 a Duniya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!