Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

 Jadawalin FIFA: Super Eagles ta koma mataki na uku a Afrika

Published

on

Tawagar Super Eagles ta koma mataki na uku a nahiyar afrika, kuma mataki na 32 a jerin kasashe da hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ke fitarwa a kowane wata.

Super Eagles a watan da ya gabata ta kasance mataki na hudu a jerin kasashe a nahiyar afrika, wanda hakan ya sanya ta samu karin matsayi a jerin kasashen.

Wanda hakan ya nuna cewa Jerin kasashen ya sa kasar Senegal da ta lashe gasar kofin afrika na AFCON na shekarar 2021 da aka buga a shekarar 2022 a kasar Kamaru itace a matakin farko, kuma ta 18 a jerin kasashe a duniya.

Yayinda kasar Moroco ta kasance a mataki na biyu, sai kuma Najeriya a mataki na uku da kuma kasar Masar wato [Egypt] da Tunisia da Kamaru da Algeria da Mali da kuma Ivory Coast da suke a jerin jadawalin na FIFA.

‘Yan wasan Super Eagles

Kasar Senegal dai ta zama zakara a gasar AFCON da aka kammala a kasar Kamaru a ranar shida ga Fabrairun shekarar 2022
Tawagar Algeria da itace ta farko a watan da ya gabata yanzu ta koma mataki na 43 a duniya, sai Mali ta 48 Ivory Coast kuma ta 51.

A jerin kasashen duniya kuma Belgium ce a matakin farko, sai Brazil, Faransa da Argentina da Ingila, Italy, Spain, Portugal, Denmark da kuma Netherlands wato Holland.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!