Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Kano Pillars ta fitar da sunayan masu horarwa 6 da za ta tantance

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, ta fitar da sunayan masu horarwa 6 dake neman aikin horar da ‘yan wasan kungiyar.

Hakan na cikin wata sanarwa da Mai magana da yawun ta Lurwanu Idris Malikawa Garu, ya fitar a yau Lahadi 29 ga Agustan shekarar 2021.

Sanarwa ta ce an zabo mutanen daga cikin masu neman aikin horar da ‘yan wasan kungiyar 25 da suka mika takardun bukatar su.

Abin da ya sa muka raba gari da mai horaswarmu – Kano Pillars

Kazalika sanarwar ta ce mutane 6 da aka fitar da sunayan na su anasaran za su zo Kano a ranar Talata 31 ga watan na Agusta, inda za su gabata a gaban kwamatin tantancewar a ranar Laraba 01 ga watan Satumba mai kamawa.

Sanarwa ta ce masu nemai aikin da aka fitar da sunayan nasu sun hadar da Busari Hakeem Ishola da Henry Makinwa da Salisu Yusuf da Erol Akay da Emanuel Amunike sai kuma Usman Shareef Abdallah.

Malikawa ya ce za’a sanar da sunan Wanda ya samu nasara da an gama tantancewar

Idan za’a iya tunawa a makon da ya gabata ne kungiyar ta Kano Pillars ta sanar da cewa, sai mai horarwar dake da lasisin hukumar kwallon kafa ta Africa CAF ne zai ci gaba da jagorantar kungiyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!