Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Ganduje ya kaddamar da rabon “Face Mask” miliyan biyu ga Kanawa

Published

on

Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya kaddamar da fara rabon takunkumin rufe baki da hanci miliyan biyu ga al’ummar jihar.

A yayin kaddamar da rabon gwamna Ganduje yace matukar al’umma zasu rika bin dokokin kariyar Corona to babu shakka za a samu saukin yaduwarta a tsakanin al’umma.

Kazalika Gwamnan yace za ayi tsari wajen rabon ta yadda kowanne kwamishina akwai karamar hukumar da zai jagoranci rabawa.

Wakiliyar Freedom Radio ta fadar gwamnatin Kano ta rawaito mana cewa gwamna Ganduje yace sakamakon rashin tsafta a unguwanni da yanka dabbobi ke janyowa gwamnati ta amince a rika bude mayankar abbatuwa a duk ranakun Litinin da Alhamis da ake sassautar dokar kulle a jihar.

Karin labarai:

Covid-19: Sanya “Face Mask” ya zama dole a Kano

Ganduje ya rabawa likitoci kayan kare kai daga Corona

Har ila yau, Zahra’u Nasir ta rawaito mana cewa kafin kaddamar da fara rabon amawalin rufe baki da hancin, gwamna Ganduje ya kaddamar da asibitin mafitsara na Abubakar Imam a matsayin cibiyar masu killace Corona da gidauniyar Dangote ta gyara ta kuma samar masa da kayayyaki.

A ranar Lahadi ne dai gwamna Ganduje ya sanar da dokar tilasta sanya amawalin rufe baki da hanci ga al’umma a jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!